Home » Gwamnonin Najeriya Za Su Gana da Hukumomin Tattalin Arziƙin Ƙasar

Gwamnonin Najeriya Za Su Gana da Hukumomin Tattalin Arziƙin Ƙasar

by Muhammad Auwal Suleiman
0 comment

Gwamnonin Jihohi 36 na Tarayyar Nijeriya za su gana da dukkan hukumomin tattalin arziki da masu samar da kudade na kasar nan, da nufin kawar da matsalolin da suka dabaibaye tsaron jihohinsu, wajen samar da ingantacciyar hanyar sarrafa kudade.

Taron wanda zai gudana a ranar Talata 4 ga watan Afrilu, bisa ga gayyatar da Darakta-Janar na ƙungiyar gwamnonin Nijeriya, Mista Asishana Bayo Okauru, ya bayar, domin tabbatar da halartar dukkan masu ruwa da tsaki cikin lamarin.

A cewar sanarwar da daraktan yada labaran kungiyar, Abdularaque Bello Barkindo, ya ce wadanda aka gayyata zuwa taron sun hada da EFCC, ICPC, Hukumar Kula da Harajin Cikin Gida ta Tarayya (FIRS) da Babban Bankin Nijeriya (CBN).

Bugu da kari, ya ce taron zai kuma yi la’akari da zurfafa gudanarwa da fadada manufofin rashin kudi wanda ya fara aiki tun daga lokacin da aka sauya fasalin kudin kasar nan, a shekarar da ta gabata.

Ya ce, Wannan taron an shirya shi ne domin nemo mafita kan matsalolin kudi.

Yace za’a shawarci dukkan gwamnoni da su bai wa taron fifiko don tattauna abubuwan da ke da nasaba da taron.

You may also like

Leave a Comment

Muhasa TVR kafa ce ta labarai mai cikakkiyar rajista wadda manufarta ita ce ilimantarwa, da wayar da kai da Inganta al’adun Hausawa da kuma nishaɗantarwa.
Muna nan a kan titin Guda Abdullahi gida mai lamba 19 a Farm Centre, jihar Kano.

Ra'ayi

Labarai da Dumi-dumi

©MuhasaTVR 2023. Ku nemi izini kafin yin amfani da duk abin da aka wallafa a wannan shafi

Are you sure want to unlock this post?
Unlock left : 0
Are you sure want to cancel subscription?