Home » Hukumar kare bayanan sirri ta yi watsi da umarnin CBN kan amfani da bayanan soshiyal midiya

Hukumar kare bayanan sirri ta yi watsi da umarnin CBN kan amfani da bayanan soshiyal midiya

by Muhammad Auwal Suleiman
0 comment
Hukumar kare bayanan sirri ta ki amincewa da umarnin CBN kan amfani bayanan soshiyal midiya

Hukumar kare bayanan sirrin masu amfani da intanet ta ƙasa (NDPC), ta ce umarnin da Babban Bankin Ƙasa (CBN) ya bai wa bankuna na neman bayanan soshiyal midiya na abokan hulɗarsu ya saɓa doka.

A ranar 26 ga Yuni ne CBN ya umarci bankuna da su riƙa karɓar bayanan soshiyal midiya na abokan hulɗarsu domin ƙara samun cikakkun bayanai game da su.

CBN ya ce hakan zai taimaka wurin yaƙi da halatta kuɗaɗen haram da kuma hada-hadar ta’addanci.

Sai dai a wata sanarwa da hukumar NDPC ta fitar ranar Alhamis ɗin nan ta ce ta na tattaunawa da CBN game da sanarwar.

You may also like

Leave a Comment

Muhasa TVR kafa ce ta labarai mai cikakkiyar rajista wadda manufarta ita ce ilimantarwa, da wayar da kai da Inganta al’adun Hausawa da kuma nishaɗantarwa.
Muna nan a kan titin Guda Abdullahi gida mai lamba 19 a Farm Centre, jihar Kano.

Ra'ayi

Labarai da Dumi-dumi

©MuhasaTVR 2023. Ku nemi izini kafin yin amfani da duk abin da aka wallafa a wannan shafi

Are you sure want to unlock this post?
Unlock left : 0
Are you sure want to cancel subscription?