Home » Shugabannin kasashen Turai sun gudanar da taro game da makomar kasar Sin a nahiyar

Shugabannin kasashen Turai sun gudanar da taro game da makomar kasar Sin a nahiyar

by Muhammad Auwal Suleiman
0 comment
Shugabannin kasashen Turai sun gudanar da taro game da makomar kasar Sin a nahiyar

A yau ne shugabannin ƙasashen Turai za su yi wani muhimmin taro a Brussels, inda ake sa ran batun China na kan gaba cikin muhimman batutuwan da za su tattauna.

Ana sa ran wasu ƙasashe mambobin ƙungiyar za su ga baiken wasu daga cikinsu da ke ci gaba da ɗasawa da Beijing ta fannin tattalin arziki musamman Faransa da Jamus, da suka bayyana aniyarsu ta ci gaba da ƙulla hulɗar kasuwanci mai karfi da Chinar.

Wannan batu dama ya jima yana haifar da rarrabuwar kawuna tsakanin ƙasashen Turan, inda da yawansu ke nuna damuwa game da dangantakar kut da kut da ke tsakanin Beijing ɗin da Rasha.

Wasu daga cikinsu kuwa na fargabar kada dogaron su ga Chinar ya haifar musu da irin raɗadin da suka ji wajen raba gari da Rasha bayan ta ƙaddamar da mamaya a Ukraine

You may also like

Leave a Comment

Muhasa TVR kafa ce ta labarai mai cikakkiyar rajista wadda manufarta ita ce ilimantarwa, da wayar da kai da Inganta al’adun Hausawa da kuma nishaɗantarwa.
Muna nan a kan titin Guda Abdullahi gida mai lamba 19 a Farm Centre, jihar Kano.

Ra'ayi

Labarai da Dumi-dumi

©MuhasaTVR 2023. Ku nemi izini kafin yin amfani da duk abin da aka wallafa a wannan shafi

Are you sure want to unlock this post?
Unlock left : 0
Are you sure want to cancel subscription?