Jirgin ƙasa ɗauke da fasinja da ya taso daga Abuja babban birnin Najeriya zuwa Kaduna ya faɗi a ranar Talata da safe.
Lamarin dai ya jefa fargaba a tsakanin fasinjoji da ke cikin jirgin.
Rahotanni na cewa lamarin ya faru ne da misalin ƙarfe 11 na safe a kauyen Asham da ke hanyar Abuja zuwa Kaduna kuma jirgin ƙasa ta bar Abuja ne da misalin karfe 9:45.
Har yanzu ba a san abin da ya jawo saukar jirgin daga kan layin dogo ba, kuma babu tabbacin ko an samu waɗanda suka jikkata.
Hukumar Jiragen ƙasa ta Najeriya (NRC) ba ta yi tsokaci a kan lamarin ba.
- ECOWAS Na Shirin Kaddamar Da Rundunar Yaƙi Da Ta’addanci
- NDLEA Ta Gano Yadda Ake Saka Kwaya A Jakunkunan Matafiya A Kano


