Kamfanin Google ya karrama dan kwallon kafar Najeriya

Kamfanin Google ya karrama marigayi dan kwallon Najeriya, Rashidi Yekini ta hanyar sanya zanensa a shafin na google a daidai lokacin da dan wasan ke cika shekaru 60 da haihuwa.

BBC ta rubuta cewa Yekini dai ya faɗa ƙangin talauci da rashin matsuguni bayan yin fice a matsayin ɗaya daga cikin manyan taurarin ƙwallon ƙafa na Najeriya.

Zanen na Google ya kwatanta murnar da Yekini ya yi lokacin da ya ci wa Najeriya ƙwallonta ta farko a gasar cin kofin duniya a 1994.

Hakan ya nuna lokacin da Yekini ya zura ƙwallo a ragar Bulgeriya, ya shige cikin ragar tare da kama ta da hannu bibbiyu yayin da hawayen murna ke kwararo masa.

Post masu alaƙa

Senegal ta lashe gasar AFCON ta 2025

CAF ta soma bincike kan hargitsin da aka samu a wasan Najeriya da Algeria

AFCON 2025: Nijeriya ta kora Aljeriya gida