Home » Kanfanin Jiragen Sama Ya Alkawurta Kwaso Daliban Najeriya Dake Sudan Kyauta

Kanfanin Jiragen Sama Ya Alkawurta Kwaso Daliban Najeriya Dake Sudan Kyauta

by Muhammad Auwal Suleiman
0 comment

A ɗaya ɓangaren kuma, kamfanin jiragen sama mai zaman kansa na Air Peace a ƙasar nan, ya bayyana aniyarsa ta kwashe ‘yan Nijeriya da rikicin kasar Sudan ya rutsa da su kyauta, idan har gwamnatin tarayya za ta iya kai su filin jirgin sama mai aminci da tsaro, a kowacce kasa da ke makwabtaka da Sudan.

An bayyana hakan ne a cikin wata sanarwa da ta fito a yau daga shugaban kamfanin kuma babban jami’in gudanarwa na kamfanin, Allen Onyema.

Ya bayyana cewa, daliban da sauran ‘yan Nijeriya wadanda suka makale a cikin kasar da ke fama da yakin, suna bukatar taimakon kamfanin cikin gaggawa.

Bai kamata ace komai gwamnati ce kadai za ta yi ba.

Onyema ya kuma kara da cewa ba sa dana sanin zama ‘yan Nigeria, saboda kalubalen da kasar ke fuskanta.

 Yace, idan aka kai daliban wata kasa, kamar Kenya ko Uganda, za su  shiga kasar don kwashe mutanenmu.

Wasu iyaye sun fara kira gare mu da mu taimaka. A shirye muke mu sake yin taimakon da muka saba yi,” inji shi.

You may also like

Leave a Comment

Muhasa TVR kafa ce ta labarai mai cikakkiyar rajista wadda manufarta ita ce ilimantarwa, da wayar da kai da Inganta al’adun Hausawa da kuma nishaɗantarwa.
Muna nan a kan titin Guda Abdullahi gida mai lamba 19 a Farm Centre, jihar Kano.

Ra'ayi

Labarai da Dumi-dumi

©MuhasaTVR 2023. Ku nemi izini kafin yin amfani da duk abin da aka wallafa a wannan shafi

Are you sure want to unlock this post?
Unlock left : 0
Are you sure want to cancel subscription?