Kano: Ƙungiyar Likitoci Musulmai Ta Ƙasa Ta Kai Tallafi Ga Ɗaurarru

Ƙungiyar likitoci musulmai na kasa ta kai tallafin kayan more rayuwa ga ɗaurarrun mutane dake gidajen gyaran hali na gwauron Dutse da Kurmawa

Shugaban kungiyar na jihar kano Dr Muhammad Auwal ya ce, suna yin aikin ne dan taimakawa marasa karfi a wurare daban daban, tare da basu kayan abinci da ruwa da makamantan su.

DA yake jawabinsa shima  Dr Anas Ibrahim Yahaya bichi wanda yana cikin tawagar   likitocin da suka duba marasa  lafiyar yace  babu kalar likitocin da babu a cikin su

Dr Muhd Lawan Adamu ya ce ko wace irin cuta suka ci karo da ita sun tanadi maganin ta

Daga karshe maimkula da gidan gyaran halin na kurmawa DC Mu’Azu Tukur wanda ya yi jawabi a madadin shugabanhukumar ya nuna godiya da jin dadin su kan aikin da kungiyar likitoci musulmi suka yi ga daurarrun.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *