Home » Kano: INEC Ta Cire Sunan Alhassan Ado Doguwa Daga Jerin Sunayen Zababbun ‘Yan Majalisa

Kano: INEC Ta Cire Sunan Alhassan Ado Doguwa Daga Jerin Sunayen Zababbun ‘Yan Majalisa

Zabe/Doguwa

by Aishatu Sule
0 comment

Hukumar Zabe ta Kasa (INEC) ta cire sunan Shugaban Masu Rinjaye na Majalisar Wakilai, Alhassan Ado Doguwa, daga jerin wadanda suka lashe zaben da aka gudanar a makon jiya.

A yayin da INEC ke shirin mika wa wadanda suka ci zaben kujerar sanata da na majalisar tarayya takardun shaida, MUHASA ta gano cewa hukumar ba ta sanya sunan Alhassan Doguwa ba a matsayin zababben dan Majalisar Tarayya na mazabar Doguwa/Tudun Wada.

Wannan na zuwa ne duk da cewa Baturen zaɓen hukumar, Farfesa Ibrahim Adamu Yakasai, ya sanar cewa Alhassan Ado Doguwa na Jam’iyyar APC ne ya lashe zaben a mazabarsa da kuri’a 39,732, a yayin da babban abokin karawarsa, Yushau Salisu Abdullahi na Jam’iyyar NNPP ya samu kuri’u 34,798. Amma a cikin jerin sunayen da INEC at fitar a daren jiya Litinin na wadanda za a mika wa shaidar cin zabe, babu sunan Alhasannan Ado Doguwa

Alhassan Ado Doguwa

Daga bisani hukumar ta bayyana cewa tursasa wa baturen zabenta aka yi ya sanar da sakamakon zaben da ke nuna dan majalisar ya lashe zaben ranar Asabar, 25 ga watan Fabrairu, 2023.

Mun yi kokarin samun karin haske daga hukumar, reshen Jahar kano ama hakan mu bai cimma ruwa ba.

You may also like

Leave a Comment

Muhasa TVR kafa ce ta labarai mai cikakkiyar rajista wadda manufarta ita ce ilimantarwa, da wayar da kai da Inganta al’adun Hausawa da kuma nishaɗantarwa.
Muna nan a kan titin Guda Abdullahi gida mai lamba 19 a Farm Centre, jihar Kano.

Ra'ayi

Labarai da Dumi-dumi

©MuhasaTVR 2023. Ku nemi izini kafin yin amfani da duk abin da aka wallafa a wannan shafi

Are you sure want to unlock this post?
Unlock left : 0
Are you sure want to cancel subscription?