Kano: Karin ɗalibai 150 sun tashi zuwa ƙasar India

Rukuni na hudu, ɗauke da ɗalibai 150 da gwamnatin Kano mai ci ta ɗauki nauyin karatunsu a ƙasashen waje sun tashi zuwa ƙasar India domin yin karatun digiri na biyu a fanni daban-daban.

Tallafin karatun na daya daga cikin manya-manyan alkawura da Gwamna Abba Kabir Yusuf ya yi lokacin yakin neman zaben sa.

Tuni dai aka fara shirin inda a yau Juma’a rukuni na huɗu ya tashi zuwa kasar India daga filin jirgin saman Malam Aminu Kano, da misalin ƙarfe 7:30 na safe.

Da yake ganawa da manema labarai jim kadan bayan tashin ɗaliban, Kwamishinan Ilimi mai Zurfi na jihar, Dr Yusuf Kofarmata, ya ce za su sauka a Legas ne kafin su wuce zuwa India.

A cewar sa, da saukar su a India, za a kwashe su zuwa jami’o’i daban-daban da za su yi karatun su a fannonin ilimi daban-daban.

Post masu alaƙa

Jigawa Za Ta Bai Wa Alhazai Abinci Sau Uku a Rana a Hajjin 2026

Namadi Ya Kaddamar da Shirin Fadada Ilimi yayin da SLU ta Yaye Dalibai Sama da 4,000

Hukumar Jin Daɗin Alhazai Ta Jigawa Ta Taya Gwamna Namadi Da Musulmi Murnar Eid-el-Fitr