Home » Kano: Za mu hukunta masu zubar da shara a wuraren da ba su kamata ba ~ Ahmadu Haruna Zago

Kano: Za mu hukunta masu zubar da shara a wuraren da ba su kamata ba ~ Ahmadu Haruna Zago

by Muhammad Auwal Suleiman
0 comment
Kano: Za mu hukunta masu zubar da shara a wuraren da ba su kamata ba ~ Ahmadu Haruna Zago

Shugaban hukumar kwashe shara da tsaftar muhalli  ta jihar Kano  Ahmadu Haruna Zago, yace hukumar sa za ta yi amfani da sashen dokar ma’aikatar wajen tursasawa tare da magance dabi’ar zubar da shara da tsakar dare a wuraren da ba su kamata ba a jihar nan.

Shugaban ya bayyana hakan ne lokacin da yake tattaunawa da manema labarai yayin da  ma’aikatan hukumar suke tsaka da aikin kwashe sharar dake fagge, ‘yan Alluna.

Dan zago yace abin takaici ne yadda wasu suke bin tsakar dare suna jibge shara akan titunan jihar nan da wuraren da basu dace ba,  musamman wuraren da aka kwashe sharar tun da farko.

A bayanansu tunda farko mazauna kasuwar ta Fagge ‘yan Alluna, sun yaba da yadda aikin kwashe sharar yake gudana a fadin jihar nan, Koda dai wasu daga cikin su sun bayyana cewa  ya kamata gwamnati ta gudanar da aikin tuntuni.

You may also like

Leave a Comment

Muhasa TVR kafa ce ta labarai mai cikakkiyar rajista wadda manufarta ita ce ilimantarwa, da wayar da kai da Inganta al’adun Hausawa da kuma nishaɗantarwa.
Muna nan a kan titin Guda Abdullahi gida mai lamba 19 a Farm Centre, jihar Kano.

Ra'ayi

Labarai da Dumi-dumi

©MuhasaTVR 2023. Ku nemi izini kafin yin amfani da duk abin da aka wallafa a wannan shafi

Are you sure want to unlock this post?
Unlock left : 0
Are you sure want to cancel subscription?