• Home  
  • Kashi 40 Na Ƴan Najeriya Na Samun wutar Lantarki Na Awa 20 A kullum – Gwamnati
- Babban Labari - Labarai

Kashi 40 Na Ƴan Najeriya Na Samun wutar Lantarki Na Awa 20 A kullum – Gwamnati

Gwamnatin tarayya ta bakin Ministan wutar lantarki Mista Adebayo Adelabu, ta bayyana cewa kaso 40 na ƴan Najeriya na samun wutar lantarki ta aƙalla awa 20 a kullum. Ministan ya yi wannan bayani ne yayin wani taro da aka yi duba akan nasarorin da ma’aikatar wutar lantarki ta samu cikin wannan shekara. A cikin wata […]

Gwamnatin tarayya ta bakin Ministan wutar lantarki Mista Adebayo Adelabu, ta bayyana cewa kaso 40 na ƴan Najeriya na samun wutar lantarki ta aƙalla awa 20 a kullum.

Ministan ya yi wannan bayani ne yayin wani taro da aka yi duba akan nasarorin da ma’aikatar wutar lantarki ta samu cikin wannan shekara.

A cikin wata sanarwa da ya fitar a ranar Lahadi, ministan yace nasarorin da suka samu a sakamakon jajircewa ne. Ministan ya ƙara da cewa dole ne Najeriya ta yi ƙoƙarin samar da wuta a koda yaushe domin samun cigaban tattalin arzikin ƙasar baki ɗaya.

“Wannan ne yasa ƙasashe irinsu China, da ƙasashen nahiyar Turai suke kan gaba wajen haɓɓakar tattalin arziƙi” a cewar  Mista Adebayo.

 

 

Game Da Mu

Gidan Radio da talabijin mai kawo muku labarai akan rukunoni daban daban. Da Hausa Muke Magana.

Yi Mana Imel: info@muhasatvr.ng

Tuntuɓi: +(234) 912 222 1000

Manyan Labarai