Home » Kashi 40 Na Ƴan Najeriya Na Samun wutar Lantarki Na Awa 20 A kullum – Gwamnati

Kashi 40 Na Ƴan Najeriya Na Samun wutar Lantarki Na Awa 20 A kullum – Gwamnati

by Mubarak Ibrahim Mandawari
0 comment

Gwamnatin tarayya ta bakin Ministan wutar lantarki Mista Adebayo Adelabu, ta bayyana cewa kaso 40 na ƴan Najeriya na samun wutar lantarki ta aƙalla awa 20 a kullum.

Ministan ya yi wannan bayani ne yayin wani taro da aka yi duba akan nasarorin da ma’aikatar wutar lantarki ta samu cikin wannan shekara.

A cikin wata sanarwa da ya fitar a ranar Lahadi, ministan yace nasarorin da suka samu a sakamakon jajircewa ne. Ministan ya ƙara da cewa dole ne Najeriya ta yi ƙoƙarin samar da wuta a koda yaushe domin samun cigaban tattalin arzikin ƙasar baki ɗaya.

“Wannan ne yasa ƙasashe irinsu China, da ƙasashen nahiyar Turai suke kan gaba wajen haɓɓakar tattalin arziƙi” a cewar  Mista Adebayo.

 

 

You may also like

Leave a Comment

Muhasa TVR kafa ce ta labarai mai cikakkiyar rajista wadda manufarta ita ce ilimantarwa, da wayar da kai da Inganta al’adun Hausawa da kuma nishaɗantarwa.
Muna nan a kan titin Guda Abdullahi gida mai lamba 19 a Farm Centre, jihar Kano.

Ra'ayi

Labarai da Dumi-dumi

©MuhasaTVR 2023. Ku nemi izini kafin yin amfani da duk abin da aka wallafa a wannan shafi

Are you sure want to unlock this post?
Unlock left : 0
Are you sure want to cancel subscription?