• Home  
  • Kungiyar ECOWAS za ta yi taron gaggawa kan juyin mulki a kasar Nijar
- Labarai

Kungiyar ECOWAS za ta yi taron gaggawa kan juyin mulki a kasar Nijar

A gobe Lahadi shugabannin Yammacin Afrika za su gudanar da wani taron gaggawa don tattaunawa kan juyin mulki da aka yi a Jamhuriyar Nijar a ranar Laraba.

Kungiyar ECOWAS za ta yi wani taron gaggawan kan juyin mulki a kasar Nijar

A gobe Lahadi shugabannin Yammacin Afrika za su gudanar da wani taron gaggawa don tattaunawa kan juyin mulki da aka yi a Jamhuriyar Nijar a ranar Laraba.

Shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu kuma sabon shugaban kungiyar ta ECOWAS, shi ne zai jagoranci zaman na ranar Lahadi wanda za a yi a Abuja, babban birnin Tarayyar Najeriya.

Shugaba Tinubu ya yi Alla-wadai da juyin mulkin a cikin wata sanarwa inda kuma ya yi wa al’ummomin kasashen waje alƙawarin cewa zai yi iyakacin ƙoƙarinsa domin kare dimokuraɗiyya da kuma tabbatar da ɗorewar kyakkyawan shugabanci a yankin.

Game Da Mu

Gidan Radio da talabijin mai kawo muku labarai akan rukunoni daban daban. Da Hausa Muke Magana.

Yi Mana Imel: info@muhasatvr.ng

Tuntuɓi: +(234) 912 222 1000

Manyan Labarai