• Home  
  • Kwankwaso na tattaunawa da jam’iyyun ADC da NDC
- Babban Labari

Kwankwaso na tattaunawa da jam’iyyun ADC da NDC

Ƙungiyar Kwankwasiyya ta tabbatar da cewa jagoran NNPP kuma ɗan takarar shugaban ƙasa a Zaɓen 2023, Rabiu Musa Kwankwaso, na ci gaba da tattaunawa da jam’iyyun ADC da kuma NDC gabanin zaɓen 2027. Mai magana da yawun ƙungiyar, Mansur Kurugu, ya shaida cewa tattaunawar na gudana ne da yiwuwar haɗa ƙarfi tsakanin ɓangarorin siyasar, duk […]

Ƙungiyar Kwankwasiyya ta tabbatar da cewa jagoran NNPP kuma ɗan takarar shugaban ƙasa a Zaɓen 2023, Rabiu Musa Kwankwaso, na ci gaba da tattaunawa da jam’iyyun ADC da kuma NDC gabanin zaɓen 2027.

Mai magana da yawun ƙungiyar, Mansur Kurugu, ya shaida cewa tattaunawar na gudana ne da yiwuwar haɗa ƙarfi tsakanin ɓangarorin siyasar, duk da cewa har yanzu ba a cimma matsaya kan wace jam’iyya za a su koma ba.

A cewarsa, “Gaskiya ne Kwankwaso na tattaunawa da ADC da NDC, kuma muna da yaƙinin cewa a ƙarshe za a zaɓi wata jam’iyya guda kafin Zaɓen 2027.”

Ya ƙara da cewa wasu manyan ‘yan siyasa da suka haɗa da Peter Obi da Seyi Makinde da kuma Seriake Dickson na daga cikin waɗanda ake tattaunawar, wadda ya ce ta yi nisa sosai.

Game Da Mu

Gidan Radio da talabijin mai kawo muku labarai akan rukunoni daban daban. Da Hausa Muke Magana.

Yi Mana Imel: info@muhasatvr.ng

Tuntuɓi: +(234) 912 222 1000

Manyan Labarai