Home » Lamiɗo Ya Zama Sarkin Ƙananan Hukumomi 3  Maimakon 8

Lamiɗo Ya Zama Sarkin Ƙananan Hukumomi 3  Maimakon 8

by Muhammad Auwal Suleiman
0 comment

Gwamantin Jihar Adamawa ta tabbatar da ta ƙwace ikon naɗa wa da tsige sarakuna daga hannun  Lamiɗon Adamawa, Alhaji Mustapha Barkinɗo ta damƙa wa Gwamnan Jihar.

Haka zalikaɓgwamnatin ta tsige Lamiɗo daga matsayinsa na Shugaban Majalisar Sarakunan Jihar na dindindin.

Majalisar Dokokin Adamawa ce dai ta yi wa dokar masarautun jihar garambawul a ranar Laraba, haka kuma ta rage ƙasar Masarautar Lamiɗon Adamawa daga ƙananan hukumomi takwas zuwa uku: Girei da Jimeta da kuma Yola.

Dokar, majalisar ta ce za ta tabbatar da adalci a tsakanin masarautun jihar da kuma kare tarihi da al’adu.

You may also like

Leave a Comment

Muhasa TVR kafa ce ta labarai mai cikakkiyar rajista wadda manufarta ita ce ilimantarwa, da wayar da kai da Inganta al’adun Hausawa da kuma nishaɗantarwa.
Muna nan a kan titin Guda Abdullahi gida mai lamba 19 a Farm Centre, jihar Kano.

Ra'ayi

Labarai da Dumi-dumi

©MuhasaTVR 2023. Ku nemi izini kafin yin amfani da duk abin da aka wallafa a wannan shafi

Are you sure want to unlock this post?
Unlock left : 0
Are you sure want to cancel subscription?