Home » Mai Shara Ya Mayar Da Miliyan 40 Da Ya Tsinta A Kano

Mai Shara Ya Mayar Da Miliyan 40 Da Ya Tsinta A Kano

by Muhammad Auwal Suleiman
0 comment

Wani mai sharar asibiti a Kano da ake kira Malam Aminu Umar Kofar Mazugal ya mayar da kudin da ya tsinta da suka kai kimanin Naira miliya 40 ga mai su.

Malam Aminu  ya tsinci kudin ne a dalolin Amurka a cikin wata jaka da mai su ya manta a Asibitin Abubakar Imam da ke unguwar Fagge a cikin birnin Kano.

Ya tsinci kudin a cikin wata jaka kuma ya mayar da kudin ga mai su, Alhaji Ahmed Abubakar, wanda ya manta da su a lokacin da ya je dubiyar mara lafiya a asibitin.

Malam Aminu ya shaida wa wakilinmu Aminiya cewa jim kadan da tafiyarsa mutumin ne shi kuma ya tsinci kudin a lokacin da yake aikin shara.

Ya ce daga bisani, bayan kimanin awa guda, mai kudin ya dawo yana cikiya, shi kuma ya mayar masa kayansa.

Shugaban Asibitin, Dokta Aminu Imam Yola, ya tabbatar da faruwar lamarin yana mai cewa hukumar gudanarwar asibitin ta sanar da Ma’aikatar Kula da Asibitoci ta Jihar Kano domin a karrama Malam Aminu.

You may also like

Leave a Comment

Muhasa TVR kafa ce ta labarai mai cikakkiyar rajista wadda manufarta ita ce ilimantarwa, da wayar da kai da Inganta al’adun Hausawa da kuma nishaɗantarwa.
Muna nan a kan titin Guda Abdullahi gida mai lamba 19 a Farm Centre, jihar Kano.

Ra'ayi

Labarai da Dumi-dumi

©MuhasaTVR 2023. Ku nemi izini kafin yin amfani da duk abin da aka wallafa a wannan shafi

Are you sure want to unlock this post?
Unlock left : 0
Are you sure want to cancel subscription?