• Home  
  • Mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima, ya kawo ziyara jihar Kano
- Labarai

Mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima, ya kawo ziyara jihar Kano

A yau ne Gwamnan jihar Kano Engr. Abba Kabir Yusuf ya karɓi baƙuncin Mataimakin Shugaban Ƙasa Alhaji Kashim Shettima.

Kashim Shettima ya ziyarci Kano ne domin kai ziyarar ta’aziyya ga iyalan marigayi dattijon jihar Alhaji Abubakar Imam Galadanchi.

Mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima, ya kawo ziyara jihar Kano

A yau ne Gwamnan jihar Kano Engr. Abba Kabir Yusuf ya karɓi baƙuncin Mataimakin Shugaban Ƙasa Alhaji Kashim Shettima.

Kashim Shettima ya ziyarci Kano ne domin kai ziyarar ta’aziyya ga iyalan marigayi dattijon jihar Alhaji Abubakar Imam Galadanchi.

A cewar wata sanarwa dauke da sa hannun sakataran yada labaran Gwamnan Kano Abba Kabir Yusuf, Sanusi Bature Dawakin Tofa, ta ce, Mataimakin Shugaban kasar zai samu tarba daga Gwamnan Jihar Kano Abba Kabir Yusuf.

Tun da sanyin Safiya dai ake ta dakon isowar Mataimakin Shugaban Ƙasar, amma har kawo lokacin haɗa wannan rahoto bai iso filin jirgin Malam Aminu Kano da ke nan Kano ba.

Game Da Mu

Gidan Radio da talabijin mai kawo muku labarai akan rukunoni daban daban. Da Hausa Muke Magana.

Yi Mana Imel: info@muhasatvr.ng

Tuntuɓi: +(234) 912 222 1000

Manyan Labarai