Home » Mataimakiyar Shugabar Amurka Ta Shelanta Ba da Tallafi Ga Mata a Afirka

Mataimakiyar Shugabar Amurka Ta Shelanta Ba da Tallafi Ga Mata a Afirka

by Muhammad Auwal Suleiman
0 comment

Mataimakiyar shugaban ƙasar Amurka Kamala Harris ta bayyana cewa samun ƙarin mata a kan karagar mulki a matsayin wani muhimmin tubali na kafa ingantacciyar dimokaradiyya.

Wannan ziyara na zuwa ne a daidai lokacin da fadar White House ta Amurka ke gudanar da taron ƙoli na dimokaridiyya karo na biyu a birnin Washington.

Harris ta ce domin samar da ingantaccen tsarin dimokuradiyya, akwai buƙatar ba wa mata damar riƙe madafun iko tare da sanya hakan ya zama ruwan dare gama duniya, ba wai wani abu da zai zama na kwatance ba.

Sannan da ta gana da mata ‘yan kasuwa da shugabanni a babban birnin kasar Ghana, inda ta yi shelar bayar da Tallafin haɗin guiwa tsakanin Gidauniyar Bill da Melinda Gates da gwamnatin Amurka na dala biliyan ɗaya ga kamfanoni masu zaman kansu don ciyar da tattalin arziki mata gaba a Afirka.

You may also like

Leave a Comment

Muhasa TVR kafa ce ta labarai mai cikakkiyar rajista wadda manufarta ita ce ilimantarwa, da wayar da kai da Inganta al’adun Hausawa da kuma nishaɗantarwa.
Muna nan a kan titin Guda Abdullahi gida mai lamba 19 a Farm Centre, jihar Kano.

Ra'ayi

Labarai da Dumi-dumi

©MuhasaTVR 2023. Ku nemi izini kafin yin amfani da duk abin da aka wallafa a wannan shafi

Are you sure want to unlock this post?
Unlock left : 0
Are you sure want to cancel subscription?