• Home  
  • Mutane 80,000 Na Buƙatar Aikin Zuciya da Huhu a Najeriya – ACTSON
- Labarai

Mutane 80,000 Na Buƙatar Aikin Zuciya da Huhu a Najeriya – ACTSON

Kungiyar Likitocin Zuciya da Huhu ta Ƙasa (ACTSON) ta ce sama da mutane 80,000 ne suke bukatar a yi musu aiki sakamakon kamuwa da ciwon zuciya kowacce shekara a fadin Najeriya.

Kungiyar Likitocin Zuciya da Huhu ta Ƙasa (ACTSON) ta ce sama da mutane 80,000 ne suke bukatar a yi musu aiki sakamakon kamuwa da ciwon zuciya kowacce shekara a fadin Najeriya.

Shugaban kungiyar, Dokta Uvie Onakpoya, ne ya bayyana hakan ranar Lahadi a Abuja, yayin babban taron kungiyar na shekara-shekara karo na biyar.

Ya lura cewa ciwon zuciya na kan gaba wajen kisan mutane a duniya, kuma adadin wadanda ke mutuwa a sakamakon shi ya haura na dukkan ragowar cututtuka baki daya.

Dokta Uvie ya ce yayin da wasu daga cikin nau’ukan cutar da su ake haifar mutum da su, wasu kuma a kan kamu da su ne dalilin kwayoyin cuta da yanayin rayuwa da hawan jini da dai sauran dalilai.

A yayin taron, Uwargidan Shugaban Kasa, Hajiya Aisha Buhari, wacce hadimarta, Dokta Victoria ta wakilta, ta ce a kwanan nan, ta dauki nauyin aikin zuciya ga yara 10 da kuma manya 13.

Game Da Mu

Gidan Radio da talabijin mai kawo muku labarai akan rukunoni daban daban. Da Hausa Muke Magana.

Yi Mana Imel: info@muhasatvr.ng

Tuntuɓi: +(234) 912 222 1000

Manyan Labarai