• Home  
  • Mutane kusan 80,000 sun rasa matsugunansu a jihar Filato
- Labarai

Mutane kusan 80,000 sun rasa matsugunansu a jihar Filato

Akalla mutane 80,000 ne suka rasa matsugunansu a cikin watanni uku sakamakon rikicin kabilanci da ya barke a jihar Filato da ke arewa maso tsakiyar Najeriya, kamar yadda wani jami’in yankin ya ce

Mutane kusan 80,000 sun rasa matsugunansu a jihar Filato

Akalla mutane 80,000 ne suka rasa matsugunansu a cikin watanni uku sakamakon rikicin kabilanci da ya barke a jihar Filato da ke arewa maso tsakiyar Najeriya, kamar yadda wani jami’in yankin ya ce, yayin da sojoji ke kara karfafa tsaro domin kawo karshen rikicin.

Tun a watan Mayun da ya gabata ne jihar Filato ta fuskanci yawaitar hare-hare a tsakanin Musulmai makiyaya da kuma al’ummar Kiristoci manoma, a rikicin da karamar hukumar ta ce ya yi sanadiyar mutuwar mutane kusan 300.

  Ko da yake Babban hafsan hafsoshin sojin Najeriya, Manjo-Janar Taoreed Lagbaja, ya ziyarci Mangu da ke jihar Filato a ranar Asabar domin fara gudanar da ayyuka na musamman don kawo karshen rikicin.

Gundumar Mangu na daya daga cikin wuraren da rikicin baya-bayan nan ya barke inda aka yi ta sace-sace a kauyuka tare da lalata filayen noma.

Game Da Mu

Gidan Radio da talabijin mai kawo muku labarai akan rukunoni daban daban. Da Hausa Muke Magana.

Yi Mana Imel: info@muhasatvr.ng

Tuntuɓi: +(234) 912 222 1000

Manyan Labarai