Home » Mutane kusan 80,000 sun rasa matsugunansu a jihar Filato

Mutane kusan 80,000 sun rasa matsugunansu a jihar Filato

by Muhammad Auwal Suleiman
0 comment
Mutane kusan 80,000 sun rasa matsugunansu a jihar Filato

Akalla mutane 80,000 ne suka rasa matsugunansu a cikin watanni uku sakamakon rikicin kabilanci da ya barke a jihar Filato da ke arewa maso tsakiyar Najeriya, kamar yadda wani jami’in yankin ya ce, yayin da sojoji ke kara karfafa tsaro domin kawo karshen rikicin.

Tun a watan Mayun da ya gabata ne jihar Filato ta fuskanci yawaitar hare-hare a tsakanin Musulmai makiyaya da kuma al’ummar Kiristoci manoma, a rikicin da karamar hukumar ta ce ya yi sanadiyar mutuwar mutane kusan 300.

  Ko da yake Babban hafsan hafsoshin sojin Najeriya, Manjo-Janar Taoreed Lagbaja, ya ziyarci Mangu da ke jihar Filato a ranar Asabar domin fara gudanar da ayyuka na musamman don kawo karshen rikicin.

Gundumar Mangu na daya daga cikin wuraren da rikicin baya-bayan nan ya barke inda aka yi ta sace-sace a kauyuka tare da lalata filayen noma.

You may also like

Leave a Comment

Muhasa TVR kafa ce ta labarai mai cikakkiyar rajista wadda manufarta ita ce ilimantarwa, da wayar da kai da Inganta al’adun Hausawa da kuma nishaɗantarwa.
Muna nan a kan titin Guda Abdullahi gida mai lamba 19 a Farm Centre, jihar Kano.

Ra'ayi

Labarai da Dumi-dumi

©MuhasaTVR 2023. Ku nemi izini kafin yin amfani da duk abin da aka wallafa a wannan shafi

Are you sure want to unlock this post?
Unlock left : 0
Are you sure want to cancel subscription?