• Home  
  • Mutum Biyu Cikin Tawagar Gwamnan Katsina Sun Rasa Ransu
- Labarai

Mutum Biyu Cikin Tawagar Gwamnan Katsina Sun Rasa Ransu

Mutum Biyu Cikin Tawagar Gwamnan Katsina Sun Rasa Ransu

Akalla mutum biyu ne suka rasa rayukansu a wani hatsarin mota da ya auku da tawagar Gwamnan Jihar Katsina, Aminu Bello Masari.

Hatsarin ya faru ne a daren ranar Juma’a a kusa da wani kauye mai suna Jimkamshi, yayin da gwamnan da tawagarsa ke hanyar zuwa Kafur, mahaifiyarsa domin jefa kuri’a a zaben gwamna da na ‘yan majalisun jihohi da ake gudanarwa a yau.

Majiyarmu ta rawaito cewa wadanda suka mutu a hatsarin sun hada da ‘yansanda guda biyu a tawagar gwamnan masu suna Kabir Adamu da Nura Safiyanu, yayin da wasu kuma suka gamu da raunuka amma suna kan samun kulawar Likitoci a asibiti.

Kodayake har zuwa lokacin da wakilinmu ke aiko da rahoton gwamnati jihar ba ta fitar da wani bayani a kan wannan hatsarin ba.

Game Da Mu

Gidan Radio da talabijin mai kawo muku labarai akan rukunoni daban daban. Da Hausa Muke Magana.

Yi Mana Imel: info@muhasatvr.ng

Tuntuɓi: +(234) 912 222 1000

Manyan Labarai