• Home  
  • Najeriya Ta Jaddada Kudirin Ta Na Inganta Samar da Abinci a Duniya A Taron UNGA80
- Babban Labari - Labarai

Najeriya Ta Jaddada Kudirin Ta Na Inganta Samar da Abinci a Duniya A Taron UNGA80

  Babban Sakataren Ma’aikatar Harkokin Noma da Samar da Abinci ta Ƙasa, Dakta Marcus Ogunbiyi, ya jagoranci tawagar Najeriya zuwa Taron Babban Zauren Majalisar Ɗinkin Duniya (UNGA) karo na 80 a Sashen Kwamiti na Biyu da ke kula da Harkokin Tattalin Arziki da Kuɗi a birnin New York. Tawagar ta Najeriya ta halarci zama na […]

 

Babban Sakataren Ma’aikatar Harkokin Noma da Samar da Abinci ta Ƙasa, Dakta Marcus Ogunbiyi, ya jagoranci tawagar Najeriya zuwa Taron Babban Zauren Majalisar Ɗinkin Duniya (UNGA) karo na 80 a Sashen Kwamiti na Biyu da ke kula da Harkokin Tattalin Arziki da Kuɗi a birnin New York.

Tawagar ta Najeriya ta halarci zama na fasaha kan noma, samar da abinci da kuma abinci mai gina jiki, inda suka jaddada aniyar Najeriya wajen taka muhimmiyar rawa a ƙoƙarin duniya na magance yunwa da rashin abinci mai gina jiki.

Dakta Ogunbiyi ya bayyana manufofi da shirye-shiryen da ake aiwatarwa a Najeriya domin ƙarfafa noma, samar da kayan aiki ga manoma, da kuma tabbatar da juriyar tsarin abinci kan matsalolin da sauyin yanayi ke haifarwa.

Ya ce, Najeriya na aiki ba kawai don tabbatar da wadatar abinci ga ‘yan ƙasa ba, har ma da taka muhimmiyar rawa wajen tsara hanyoyin dorewa don magance ƙalubalen samun abinci a duniya.

Game Da Mu

Gidan Radio da talabijin mai kawo muku labarai akan rukunoni daban daban. Da Hausa Muke Magana.

Yi Mana Imel: info@muhasatvr.ng

Tuntuɓi: +(234) 912 222 1000

Manyan Labarai