Najeriya na fatan cewa damarta ta zuwa gasar Kofin Duniya a baɗi na nan, bayan gabatar da ƙorafi da ta yi wanda ke zargin cewa Jamhuriyar Dimokraɗiyyar Kongo ta saka ƴan wasan da ba su cancanta ba a ƙarawa da suka yi a wasan ƙarshe na ƙasashen Afirka masu neman gurbin zuwa kofin duniya na 2026 a watan da ya gabata.
Kongo ta doke Najeriya a bugun fenariti don samun damar zuwa wasan gurbi na ƙasashe daga nahiyoyi da za a yi a watan Maris na shekara mai zuwa, wanda zai bai wa ƙasa damar zuwa gasar da za a yi a ƙasashen Canada, Mexico da kuma Amurka.

