Home » Netumbo Nandi Ta Zama Mace Ta Farko Da Zata Jagoranci Shugancin Kasar Namibia

Netumbo Nandi Ta Zama Mace Ta Farko Da Zata Jagoranci Shugancin Kasar Namibia

by Mujahid Wada Guringawa
0 comment

An rantsar da Netumbo Nandi-Ndaitwah a matsayin shugabar ƙasar Namibia, wadda ta kafa tarihin zama mace ta farko da za ta jagoranci ƙasar.

Tshohuwar ministar harkokin wajen ƙasar ta kasance jajirtaciyyar ƴar jam’iyyar SWAPO wadda ke mulkin Namibia tun bayan samun ƴancin kai daga Afirka ta Kudu a 1990.

Da take magana da BBC, Nandi-Ndaitwah ta yarda da cewa wasu za su iya sukarta saboda jinsinta maimakon ayyukan da take yi – sai dai ta ce za ta ci gaba da yaƙi da cin zarafin jinsi.

Netumbo ta shiga cikin jerin matan Afirka ƙalilan da suka jagoranci ƙasarsu tun lokacin da Liberia ta zaɓi shugabar ƙasa ta mace ta farko shekaru 20 da suka wuce.

You may also like

Leave a Comment

Muhasa TVR kafa ce ta labarai mai cikakkiyar rajista wadda manufarta ita ce ilimantarwa, da wayar da kai da Inganta al’adun Hausawa da kuma nishaɗantarwa.
Muna nan a kan titin Guda Abdullahi gida mai lamba 19 a Farm Centre, jihar Kano.

Ra'ayi

Labarai da Dumi-dumi

©MuhasaTVR 2023. Ku nemi izini kafin yin amfani da duk abin da aka wallafa a wannan shafi

Are you sure want to unlock this post?
Unlock left : 0
Are you sure want to cancel subscription?