Home » NNPC Ta sanar da komawa Haƙar Man Fetur a Jihar Barno

NNPC Ta sanar da komawa Haƙar Man Fetur a Jihar Barno

by Muhammad Auwal Suleiman
0 comment
NNPC ya sanar da komawa aikin laluben da ake zaton samu a jihar Borno

Kamfanin mai na Najeriya NNPC ya sanar da komawa aikin neman mai a yankin Tafkin Chadi da ke jihar Borno.

Kamfanin ya dakatar da aikin ne a watan Yuli na shekara ta 2017, bayan da wasu mahara da ake zargin ‘yan Boko Haram ne suka kai wa ma’aikatan hari har suka yi garkuwa da wasu.

Shugaba Muhammadu Buhari ya gabatar da jawabi ta intanet ga taron kaddamar da komawa kan aikin gano man a wata rijiya da ke yankin Wadi-B a garin Tuba na karamar hukumar Jere.

Kamfanin ya ce yana da kyakkyawan zato cewa za a samu mai da gas mai yawan gaske a wannan wuri.

You may also like

Leave a Comment

Muhasa TVR kafa ce ta labarai mai cikakkiyar rajista wadda manufarta ita ce ilimantarwa, da wayar da kai da Inganta al’adun Hausawa da kuma nishaɗantarwa.
Muna nan a kan titin Guda Abdullahi gida mai lamba 19 a Farm Centre, jihar Kano.

Ra'ayi

Labarai da Dumi-dumi

©MuhasaTVR 2023. Ku nemi izini kafin yin amfani da duk abin da aka wallafa a wannan shafi

Are you sure want to unlock this post?
Unlock left : 0
Are you sure want to cancel subscription?