Home » Rikicin Shugabanci:- Gwamnatin Kano Ta Rushe Shugabancin Hukumar Kare Hakkin Masu Siyan Kayayyaki

Rikicin Shugabanci:- Gwamnatin Kano Ta Rushe Shugabancin Hukumar Kare Hakkin Masu Siyan Kayayyaki

Gwamnan jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusif, ya rushe shugabancin hukumar kare hakkin masu siyan kayayyaki ta Jihar wato (Consumer Protection Council) dukkan su saboda ricikin shugabanci .

by Mujahid Wada Guringawa
0 comment

Gwamnan jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusif, ya rushe shugabancin hukumar kare hakkin masu siyan kayayyaki ta Jihar wato (Consumer Protection Council) dukkan su saboda ricikin shugabanci .

Sakataren gwamnatin Jihar Kano, Alhaji Umar Faruk Ibrahim, ne ya sanar da hakan ta cikin wata sanarwa da daraktan yada labaran sa ya fitar, inda ya ce matakin ya biyo bayan dogon rikicin shugabancin da ya dabaibaye hukumar, duk da kokarin da aka yi wajen tabbatar da zaman lafiya, a hukumar amma hakan bata samu ba.

A cewar, “Bisa umarnin gwamna Abba Kabir Yusif, Shugaban hukumar, da Sakataren Zartarwa da dukkan mambobi, ciki har da mambobin Ex-Officio, duk an rushe su nan take”.

Umar Faruk, ya kuma umarci dukkan jami’an da abin ya shafa su mika ragamar aiki tare da dukkan kayayyakin gwamnati da ke hannunsu ga jami’in da ya fi kowa matsayi a hukumar, a ranar Litinin, 27 ga watan Oktoban 2025.

A ƙarshe sanarwar ta ce gwamnatin Jihar Kano za ta ci gaba da daukar matakai don tabbatar da ingantaccen shugabanci, da gaskiya, da kyakkyawan shuganci a hukumominta.

You may also like

Leave a Comment

Muhasa TVR kafa ce ta labarai mai cikakkiyar rajista wadda manufarta ita ce ilimantarwa, da wayar da kai da Inganta al’adun Hausawa da kuma nishaɗantarwa.
Muna nan a kan titin Guda Abdullahi gida mai lamba 19 a Farm Centre, jihar Kano.

Ra'ayi

Labarai da Dumi-dumi

©MuhasaTVR 2023. Ku nemi izini kafin yin amfani da duk abin da aka wallafa a wannan shafi

Are you sure want to unlock this post?
Unlock left : 0
Are you sure want to cancel subscription?