Home » Sabon Shugaban Ƙasa, Tinubu, Ya Tafi Hutu Turai da Umrah

Sabon Shugaban Ƙasa, Tinubu, Ya Tafi Hutu Turai da Umrah

by Muhammad Auwal Suleiman
0 comment

Sabon zaɓaɓɓen shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya bar ƙasar nan zuwa wasu ƙasashen Turai domin hutu, inda daga can kuma zai zarce ƙasar Saudiyya domin aikin Umrah.

Kakakin zaɓaɓɓan shugaban ƙasar Tunde Rahman ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar.

A cikin sanarwar kakakin ya ce, Tinubun ya fita ne domin ya je ya huce gajiyar yakin neman zabe da kuma harkokin zaben sannan kuma ya tsara shirinsa na karbar mulki kafin ranar kaddamarwarsa ta 29 ga watan Mayu na shekarar nan ta 2023.

Tunde ya ce zaɓaɓɓen shugaban ya nufi nahiyar Turai, inda zai je ƙasar Faransa da kuma London domin ya huta, sannan kuma ya wuce ƙasar Saudiyya domin ibadar Umrah da kuma azumin watan Ramadana.

You may also like

Leave a Comment

Muhasa TVR kafa ce ta labarai mai cikakkiyar rajista wadda manufarta ita ce ilimantarwa, da wayar da kai da Inganta al’adun Hausawa da kuma nishaɗantarwa.
Muna nan a kan titin Guda Abdullahi gida mai lamba 19 a Farm Centre, jihar Kano.

Ra'ayi

Labarai da Dumi-dumi

©MuhasaTVR 2023. Ku nemi izini kafin yin amfani da duk abin da aka wallafa a wannan shafi

Are you sure want to unlock this post?
Unlock left : 0
Are you sure want to cancel subscription?