Gwamnan jihar Jigawa Malam Umar Namadi FCA, ya karbi bakuncin sarakunan jihar su biyar, wadanda uku daga cikinsu suka samu wakilcin hakimansu karkashin jagorancin shugaban majalissar sarakuunan jihar, Mai Martaba Alhaji Adamu Abubakar Make Haruna CON Sarkin Hadejia.
Ziyarar sarakunan na zuwa ne bayan dawowar gwamna Namadi Umar, daga bikin karbar lambar yabon da ya samu ta jaridar Leadership, kan iya shugabanci da aiyukan raya kasa wanda aka gudanar a dakin taro na Banquet Hall dake fadar shugaban kasa a birnin tarayya Abuja.
Haka zalika sarakunan sun yi masa barka da kamamala bukukuwan salla , kamar yadda aka saba bisa al’adun sarakuunan ga kowacce gwamnati bayan kammala bikin salla suke ziyartar gwamna.
Shugaban majalissar sarakuunan jihar, mai martaba Sarkin Hadejia, HRH Adamu Abubakar Maje CON , ya yabawa gwamnan jihar bisa kokarin da yake yi musamman wajen magance matsalolin tsaro da kuma kafa kwamiti na musamman kan kawo karhsen rikicin manoma da makiyaya a jihar.
- Kisan Uromi: Gwamnatin Tarayya Ta Kafa Kwamitin Bincike Kan Kisan Matafiya A Edo
- NAPTIP Ta Kaddamar Da Sabbin Hanyoyin Yaki Da Safarar Mutane
Sarakuunan sun kuma yabawa masa na shirya taron masalaha tare da cin abinci da manoma da makiyaya wanda akayi a kwanakin baya tare da jaddada godiyarsu bisa sanya hakimansu da sauran wakilansu cikin kwamitin gudanar da aikin gina sabbin cibiyoyin wankin Koda, a masarautun jihar guda 5 wadanda tuni aka fara gudanar da aikin don magance matsalolin ciwon koda a jihar Jigawa
Haka zalika mai martaba sarkin Hadejia , a madadin sarakunan jihar , ya yi kira ga al’umma su ci gaba da bawa gwamnatin Malam Umar Namadi goyon baya ¸ tare da yi masa addu’o’in samun nasarar aiwatar da muhimman aiyukan raya kasa daya sanya a gaba a fadin jihar.
Daya jawabi gwamna Umar Namadi , ya yabawa sarakunan bisa goyon bayan da suke bashi wajen aiwatar da aiyuka a fadin jihar.