Home » ‘Yan Sanda Sun Kamo ‘Yan Daba A Kano

‘Yan Sanda Sun Kamo ‘Yan Daba A Kano

by Mujahid Wada Guringawa
0 comment

Rundunar ‘yan sandan Najeriya reshen jihar Kano ta kama mutane 8 cikin wadanda ake zargi sun fito fadan daba tare da jiwa Kansu raunuka, a unguwar kofar Na’isa ranar Alhamis din data gabata.

Kakakin rundunar ƴan sandan jihar Kano, SP Abdullahi Haruna Kiyawa, ne ya bayyana a shafin sa na Facebook , ayau Asabar.

Rundunar yan sandan ta kuma bayyana damuwa, kan yadda matasan da suka samu raunukan, suka ki sanarwa da yan sanda, don kaisu asibiti a kula da lafiyarsu.

Kiyawa ya kara da cewa jami’an yan sanda sun shiga cikin unguwar, tare da mutane 8 da raunuka a jikinsu da kuma Wukake.

Sanarwar ta ce ana ci gaba da gudanar da bincike don kamo sauran wadanda ake zargi da aikata laifukan.

A ranar Alhamis din data gabata ne , wasu matasa da ake zargin Yan daba ne suka fito,Inda suka tayar da hankalin mazauna yankin da makotansu.

You may also like

Leave a Comment

Muhasa TVR kafa ce ta labarai mai cikakkiyar rajista wadda manufarta ita ce ilimantarwa, da wayar da kai da Inganta al’adun Hausawa da kuma nishaɗantarwa.
Muna nan a kan titin Guda Abdullahi gida mai lamba 19 a Farm Centre, jihar Kano.

Ra'ayi

Labarai da Dumi-dumi

©MuhasaTVR 2023. Ku nemi izini kafin yin amfani da duk abin da aka wallafa a wannan shafi

Are you sure want to unlock this post?
Unlock left : 0
Are you sure want to cancel subscription?