Home » Sarkin Musulmi III ya buƙaci ƙungiyar ƙwadago ta janye shiga yajin aiki

Sarkin Musulmi III ya buƙaci ƙungiyar ƙwadago ta janye shiga yajin aiki

by Muhammad Auwal Suleiman
0 comment
Sarkin Musulmi III ya buƙaci ƙungiyar ƙwadago ta janye shiga yajin aiki

Mai alfarma Sarkin Musulmi kuma Shugaban Majalisar Koli a Harkokin Addinin Musulunci, Alhaji Sa’ad Abubakar na uku, ya yi kira ga ƙungiyoyin ƙwadago da su janye batun yajin aiki da zasu shiga a faɗin ƙasar daga ranar Talata 3 ga watan Oktoba.

Sarkin ya bayyana hakan ne a wajen bude taron shirya bikin cikar ƙasar nan shekaru 63 da samun ‘yancin kai wanda ya gudana a jiya Juma’a a birnin tarayya Abuja.

Ya jaddada buƙatar tattaunawa don nemo mafita kan batutuwan maimakon fara yajin aikin ko don maslahar talakawa.

A ƙarshe ya ce yana mai bayar da shawarar tattaunawa ne saboda yajin aikin ba zai magance matsalolin ƙasar nan ba.

You may also like

Leave a Comment

Muhasa TVR kafa ce ta labarai mai cikakkiyar rajista wadda manufarta ita ce ilimantarwa, da wayar da kai da Inganta al’adun Hausawa da kuma nishaɗantarwa.
Muna nan a kan titin Guda Abdullahi gida mai lamba 19 a Farm Centre, jihar Kano.

Ra'ayi

Labarai da Dumi-dumi

©MuhasaTVR 2023. Ku nemi izini kafin yin amfani da duk abin da aka wallafa a wannan shafi

Are you sure want to unlock this post?
Unlock left : 0
Are you sure want to cancel subscription?