• Home  
  • Shugaban Hukumar kwallon Ƙafa ta Najeriya Ibrahim Gusau ya yi murabus
- Wasanni

Shugaban Hukumar kwallon Ƙafa ta Najeriya Ibrahim Gusau ya yi murabus

Shugaban Hukumar Kwallon Ƙafa ta Najeriya, NFF, Ibrahim Gusau ya yi murabus daga muƙamisa. Gusau ya shaida haka ne a yau Alhamis a shedikwatar Hukumar Kwallon Kafa ta kasar a wani taron manema labarai. An ta suka kan yadda tawagogin Najeriya na mata da maza suka gaza ƙoƙari a ‘yan shekarun bayan nan, ciki har […]

Shugaban Hukumar Kwallon Ƙafa ta Najeriya, NFF, Ibrahim Gusau ya yi murabus daga muƙamisa.

Gusau ya shaida haka ne a yau Alhamis a shedikwatar Hukumar Kwallon Kafa ta kasar a wani taron manema labarai.

An ta suka kan yadda tawagogin Najeriya na mata da maza suka gaza ƙoƙari a ‘yan shekarun bayan nan, ciki har da gaza samun gurbi a gasar kofin duniya.

Rahotanni sun ce hukumomin Najeriya na bincike kan hukumar ta NFF game da yadda ta kashe wasu kuɗaɗe naira 17bn don biyan albashi da sauran hidimar ‘yan wasa.

A bangaren wasannin cikin gida kuma an yi zargin cewa alkalan wasa ba su samu kudadensu ba tun daga mako na 25 zuwa mako na 38, da dai sauran wasu korafe-korafe.

Game Da Mu

Gidan Radio da talabijin mai kawo muku labarai akan rukunoni daban daban. Da Hausa Muke Magana.

Yi Mana Imel: info@muhasatvr.ng

Tuntuɓi: +(234) 912 222 1000