• Home  
  • Sojojin Najeriya sun ceto mutane 9 daga masu garkuwa a Kogi.
- Labarai

Sojojin Najeriya sun ceto mutane 9 daga masu garkuwa a Kogi.

Sojojin Najeriya sun ceto mutane tara, ciki har da jariri, bayan arangama da wasu da ake zargin masu garkuwa da mutane ne a kan hanyar Ajaokuta zuwa Itobe a Jihar Kogi. Dakarun Bataliya ta 21 sun bi sawun masu garkuwar har zuwa kusa da Adumu, inda suka yi musu luguden wuta, lamarin da ya tilasta […]

Sojojin Najeriya sun ceto mutane tara, ciki har da jariri, bayan arangama da wasu da ake zargin masu garkuwa da mutane ne a kan hanyar Ajaokuta zuwa Itobe a Jihar Kogi.

Dakarun Bataliya ta 21 sun bi sawun masu garkuwar har zuwa kusa da Adumu, inda suka yi musu luguden wuta, lamarin da ya tilasta musu tserewa tare da barin wadanda suka yi garkuwa da su.

Daga cikin wadanda aka ceto akwai tsofaffi maza biyu, tsofaffi mata biyu, maza hudu da jariri.

An mika wadanda aka ceto ga yan sanda a Itobe, yayin da sojojin ke ci gaba da neman sauran wadanda ake zargin an yi garkuwa da su.

 

Game Da Mu

Gidan Radio da talabijin mai kawo muku labarai akan rukunoni daban daban. Da Hausa Muke Magana.

Yi Mana Imel: info@muhasatvr.ng

Tuntuɓi: +(234) 912 222 1000

Manyan Labarai