Home » Sojojin Sudan Na Daf Da Kwace Fadar Shugaban Kasa Daga Dakarun RSF – Gidan Talabijin Na Sudan

Sojojin Sudan Na Daf Da Kwace Fadar Shugaban Kasa Daga Dakarun RSF – Gidan Talabijin Na Sudan

Jaridar TRT Hausa ta  bayyana cewa Gidan talbijin na Sudan ranar Alhamis ya ce sojojin ƙasar na dab da karɓe iko da Fadar shugaban ƙasar a Khartoum daga hannun dakarun rundunar RSF, lamarin da ya kawo wani babban sauyi a yaƙin da aka yi shekara biyu ana gwabzawa wanda yake barazanar raba ƙasar.

by Muhammad Auwal Suleiman
0 comment

Jaridar TRT Hausa ta  bayyana cewa Gidan talbijin na Sudan ranar Alhamis ya ce sojojin ƙasar na dab da karɓe iko da Fadar shugaban ƙasar a Khartoum daga hannun dakarun rundunar RSF, lamarin da ya kawo wani babban sauyi a yaƙin da aka yi shekara biyu ana gwabzawa wanda yake barazanar raba ƙasar.

A yammacin ranar Laraba, an yi musayar wuta a kusa da fadar shugaban ƙasar, inda aka ji fashewar abubuwa da kuma hare-haren sama da sojin ta kai tsakiyar Khartoum, kamar yadda shaidu da kamfanin dillancin labaran Reuters suka ruwaito.

Ɓangarorin biyu na soji sun yi juyin mulki a shekarar 2021, lamarin da ya katse shirin miƙa mulki ga farar-hula, kuma yaƙi ya ɓarke a watan Afrilun shekarar 2023 bayan wani sabon shirin miƙa mulki ga farar-hula ya janyo rikici.

Yaƙin ya janyo abin da Majalisar Ɗinkin Duniya (MDD) ke kira matsalar jinƙai mafi girma a duniya da kuma ƙeta haƙƙin ɗan’adam mai yawa.

You may also like

Leave a Comment

Muhasa TVR kafa ce ta labarai mai cikakkiyar rajista wadda manufarta ita ce ilimantarwa, da wayar da kai da Inganta al’adun Hausawa da kuma nishaɗantarwa.
Muna nan a kan titin Guda Abdullahi gida mai lamba 19 a Farm Centre, jihar Kano.

Ra'ayi

Labarai da Dumi-dumi

©MuhasaTVR 2023. Ku nemi izini kafin yin amfani da duk abin da aka wallafa a wannan shafi

Are you sure want to unlock this post?
Unlock left : 0
Are you sure want to cancel subscription?