An kammala tattaunawar sulhu tsakanin Amurka da Iran
Tawagar manyan jamai’an Iran da Amurka sun yi zaman tattaunawar sulhu ta sa’o’i biyu a birnin Islamabad. Ba a sanar da matsayar zaman ba, amma wakilin BBC ya ce amincewar bangarorin biyu su yi ganawar kai tsaye alama ce ta nasara. Kafar yaɗa labaran Iran ta ce za a ƙara wata tattaunawar a ƙarshen mako. […]