Babban Labari
Labarai
Wani Ya Maka ‘Yan Kwamitin Unguwa A Kotu Saboda Sun Hana Shi Zuwa Hira Wurin Bazawararsa.
Wani mutum mai suna Yusif Musa ya shigar da ƙara a gaban kotun shari’ar Musulunci da ke Danbare, ƙarƙashin jagorancin Alkali Munzali Idris Gwadabe, yana zargin shugaban kwamitin unguwar Yankusa, Abdulaziz Isa, da hana shi zuwa zance wajen wata bazawara da suke soyayya da ita, mai suna Amira Abubakar.

