Babban Labari
DSS ta sake gurfanar da El-Rufai kan zargin satar bayanai ta wayar Ribadu
Hukumar tsaron farin kaya ta DSS ta sake gurfanar da tsohon gwamnan jihar Kaduna, Nasir El-Rufai, a gaban Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja kan zargin sauraron kiran waya na mai bai wa shugaban ƙasa shawara kan harkokin tsaro (NSA). An kawo El-Rufai kotun da misalin ƙarfe 8:55 na safiyar Litinin tare da jami’an DSS […]

