Babban Labari
Labarai
An Kama Mutane 9 Bayan Rikici Ya Ɓarke Kan Kisan Ɗan Acaɓa a Garko
Rundunar ’Yan Sanda ta Jihar Kano ta ce ta fara cikakken bincike kan zargin kisan wani ɗan acaɓa da aka yi a karamar hukumar Garko, da kuma rikicin da ya biyo bayan kama waɗanda ake zargi da hannu a lamarin.

