Ana Zargin Wani Mutum Da Kashe Matar Kaninsa Da Kuma Raunata Yarinya A Jigawa
Rundunar ƴansanda a jihar Jigawa sun ce sun kama wani mutum bisa zargin kashe matar ƙaninsa a ƙauyen Gunka da ke karamar hukumar Jahun a jihar. Wata sanarwa da kakakin ƴansandan jihar SP Lawan Shiisu Adam ya fitar ranar Alhamis, ya ce ana zargin mutumin mai suna Buhari Sule mai shekara 25 da far wa […]