Gwamanatin Jigawa Za Ta Taimaki Masu Bincike Akan Ciwon Ƙoda

Gwamnatin jihar Jigawa ta yi alƙawarin taimakawa masana masu bincike akan ciwon ƙoda da ke addabar jama’ar wasu yankuna a jihar. 

Kwamishinan lafiya a ji Jigawa, Honorabul Dokta Muhammad Abdullahi Kainuwa ne ya bayyana hakan a wani taron wayar da kai akan ciwon ƙoda a Haɗejia.

Kungiyar Likitoci ta Najeriya ne dai ta shirya taron a garin Haɗejia, ɗaya daga cikin yankunan da ke fama da samun mutane masu ciwon ƙoda.

Kainuwa ya bayyana cewa zai yi amfani da damarsa, wurin haɗa masu niyyar yin bincike mai zurfi akan ciwon ƙoda da waɗanda za su ɗauki nauyin binciken.

Ya ce zurfafa bincike akan ciwon ƙoda zai taimaka wurin magance ciwon cikin gaggawa.

Post masu alaƙa

Ƴan sandan Kano za su ƙara ƙaimi wajen amsa kiran gaggawa – CP Bakori

Masu Garkuwa Da Janar Rabe Na Neman A Sako ’Yan Bindigar Da Ke Hannun Gwamnati

Gwamna Namadi ya dakatar da hadimansa huɗu