Gwamanatin Jigawa Za Ta Taimaki Masu Bincike Akan Ciwon Ƙoda

Gwamnatin jihar Jigawa ta yi alƙawarin taimakawa masana masu bincike akan ciwon ƙoda da ke addabar jama’ar wasu yankuna a jihar. 

Kwamishinan lafiya a ji Jigawa, Honorabul Dokta Muhammad Abdullahi Kainuwa ne ya bayyana hakan a wani taron wayar da kai akan ciwon ƙoda a Haɗejia.

Kungiyar Likitoci ta Najeriya ne dai ta shirya taron a garin Haɗejia, ɗaya daga cikin yankunan da ke fama da samun mutane masu ciwon ƙoda.

Kainuwa ya bayyana cewa zai yi amfani da damarsa, wurin haɗa masu niyyar yin bincike mai zurfi akan ciwon ƙoda da waɗanda za su ɗauki nauyin binciken.

Ya ce zurfafa bincike akan ciwon ƙoda zai taimaka wurin magance ciwon cikin gaggawa.

Post masu alaƙa

Sojojin Najeriya sun daƙile yunƙurin garkuwa da mutane tare da ceto mutum 23

Dan KAROTA da direba ya buge ya gudu Nasiru Abdullahi Mai Jihadi ya rasu ya bar mata 2 da ‘ya’ya 12.

An kama budurwa ‘yar shekara 15 kan safarar miyagun kwayoyi a Delta.