jigawa

Gwamnati za ta mayar da yara 5,000 makaranta a Jigawa

Gwamnatin Tarayya ta fara gudanar da shirin tantance matakin ilimin ɗalibai a faɗin ƙasar nan domin duba yadda ɗalibai ke fahimtar abin da ake koya musu, tare da amfani da sakamako wajen tsara manufofi da shirye-shiryen bunƙasa ilimi. Ƙaramar Ministar Ilimi, Farfesa Suwaiba Sa’id Ahmad ce ta bayyana hakan yayin da ta kai ziyarar duba […]

Read more

Gwamna Namadi ya dakatar da hadimansa huɗu

Gwamna Umar Namadi na Jihar Jigawa, ya dakatar da wasu hadimansa huɗu daga aiki har sai abin da hali ya yi. Wata sanarwa da Sakataren Gwamnatin Jihar, Malam Bala Ibrahim, ya fitar a ranar Litinin ta ce dakatarwar ta fara aiki nan take. Waɗanda abin ya shafa sun haɗa da Abbas Makama, Babban Mataimaki na […]

Read more

Babandede Ya Ziyarci Iyalan Hon. Laushi, Ya Ba Su Tallafi

Shugaban hukumar shigi da fici ta Najeriya mai ritaya kuma jigo a jam’iyyar APC, Muhammad Babandede, ya ziyarci iyalan tsohon ɗan majalisar wakilai, Hon. Abba Anas Adamu Laushi, wanda ya rasu a hannun masu garkuwa da mutane. Babandede ya bayyana rasuwar marigayin a matsayin babban rashi ga iyalansa, al’ummarsa da kuma abokan siyasarsa, yana mai […]

Read more

Ƴan sanda sun tsaurara tsaro a cibiyoyin JAMB jihar a Jigawa

Kwamishinan ƴan sandan Jihar Jigawa, CP Haruna A. Yahaya, ya kai ziyara cibiyoyin rubuta jarrabawar JAMB, don duba  yanayin tsaron wuraren da ake gudanar jarrabawar. Ziyarar tasa na da nufin tabbatar da cewa an gudanar da jarrabawar cikin kwanciyar hankali da lumana da kuma bin tsari, ba tare da an samu wata matsala ba. Kakakin […]

Read more