Jirgin Ruwa Ya Yi Ajalin Mutane Biyar A Nahuche, Jihar Jigawa
Jirgin Ruwa ya yi ajalin mutane 5 a garin Nahuche Karamar Hukumar Taura Jihar Jigawa.
Jirgin Ruwa ya yi ajalin mutane 5 a garin Nahuche Karamar Hukumar Taura Jihar Jigawa.
Rundunar ƴan sandan Najeriya a jihar Jigawa ta ce an samu mummunan rikici tsakanin manoma da makiyaya a ƙaramar hukumar Birnin Kudu. An ce lamarin ya yi sanadin mutuwar mutum biyu da ƙona wasu gidaje uku. ‘Yan sandan sun ce sun kama mutum biyar da hannu a afkuwar rikicin, inda ake ci gaba da gudanar […]
Gwamna Umar A. Namadi, ya amince da naɗin Farfesa Muhammad Ibrahim Yakasai, a may sabon shugaban jami’ar Sule Lamiɗo, Kafin Hausa (SLU) Wannan amincewa na ƙunshe ne a cikin jawabin da sakataren gwamnatin jihar, Malam Bala Ibrahim, ya fitar. Sannan ya yi ƙarin haske da cewa naɗin nasa ya biyo bayan miƙo sunansa da […]
A ranar Talata 7 ga watan Nuwamban shekarar 2023 aka yi jana’izar mai girma Magajin Rafin Hadejia, Alhaji Mohammadu Babandede Sarkiki, mahaifi ga Muhammad Babandede, tsohon shugaban hukumar shigi da fici ta ƙasa
Shugaban ƙaramar hukumar Honarabul Nasiru Ahmed Kiyawa – wanda ya tabbatar wa da BBC faruwar lamarin – ya ce ‘yan bindigar sun je gidan nasa ne bayan sallar isha’i a ranar Juma’a daddare, inda suka kore mutanen da ke kofar gidan nasa kafin su shiga ciki.
Gwamnatin jihar Jigawa ta tabbatar da cewa ta yi nasarar yashe kogin Hadeja a tazarar da ta kai kilomita 60 tare da gina katangar kariya a tsawon kilomita 100 domin magance matsalar ambaliyar ruwa da ake samu a jihar.
Hukumar ba da agajin gaggawa ta kasa wato NEMA ta kai tallafi ga kauyuka biyu da suka gamu da annobar gobara a karamar hukumar kiyawa dage Jahar jigawa