NEMA: Ta Kai Ɗauki Jihar Jigawa

Hukumar ba da agajin gaggawa ta kasa wato NEMA  ta kai tallafi ga kauyuka biyu da suka gamu da annobar gobara a karamar hukumar kiyawa dage Jahar jigawa

Shugaban hukumar ta NEMA Mustafa Habib ya ce sun kawo kayan tallafi ne bisa umarnin ministar ba da tallafin jinkai Sadiyar Umar Faruk bisa sahalewar shugaban kasa muhammau Buhari .

Da yake amsar kayan tallafin, mataimakin gwamnan Jahar ta jigawa Umar Namadi,ya yaba wa shugaban hukumar da ta ba da agajin gaggawa da kuma ministar ba da tallafin jinkai da kuma uwa uba shugaban kasa Muhammad Buhari.

Idan dai za iya tunawa a ranar Alhamis din da ta gabata ne dai wata gobara da ta tashi a kauyukan malamawa da karangiya  dake karamar hukumar kiyawa ta Jahar jigawa wacce ta yi sanadiyar kona dukiyoyi da dama.

Ko da a nan Jihar Kano an samu makamanciyar irin wannan gobara a kasuwar Rimi da ke nan Kano waɗana ake sa ran su ma tuni sun samu makamanciyar wannan tallafi.

Post masu alaƙa

Jigawa Za Ta Bai Wa Alhazai Abinci Sau Uku a Rana a Hajjin 2026

Namadi Ya Kaddamar da Shirin Fadada Ilimi yayin da SLU ta Yaye Dalibai Sama da 4,000

Hukumar Jin Daɗin Alhazai Ta Jigawa Ta Taya Gwamna Namadi Da Musulmi Murnar Eid-el-Fitr