Tag: Nigeria

Babban Labari Labarai

Kungiyar Likitocin Nijeriya Ce Zata Tantance Sahihancin Rashin Lafiyar Nnamdi Kadu: Kotu

Babban Kotun Tarayya ta daƙile buƙatar Nnamdi Kanu na neman a kai shi asibiti, inda ta umarci shugaban ƙungiyar likitocin Najeriya (NMA) ya kafa kwamitin likitoci tsakanin takwas zuwa goma domin tantance lafiyar shugaban ƙungiyar IPOB da ya ke ikirarin fama da rashin lafiya mai tsanani. Mai shari’a James Omotosho ne ya bayar da wannan […]

Babban Labari Labarai

Ana Zargin Jika Da Halaka Kakanninsa A Kano

Yanzu haka ana zargin wani matashi mai suna Mutawakilu Ibrahim, dan shekara kusan 30 mazaunin unguwar Kofar Dawanau, ya halaka kakanninsa biyu ta hanyar caka mu su wuka dake jihar Kano. Wani makocin mamatan biyu Malam Mukhtar Harisu ya tabbatarwa da tashar Muhasa TV da Rediyo cewa, lamarin ya faru ne da misalin karfe 9 […]

Babban Labari Labarai

An Kama Yan Nijeriya 106 Da Zargin Safarar Miyagun Kwayoyi A India

Hukumomi a Indiya sun tuhumi ‘yan Najeriya 106 da laifin safarar miyagun ƙwayoyi a shekarar 2024 da ta gabata, kamar yadda jaridar Indian Express ta ruwaito. Rahoton ya ce ‘yan Najeriyar na cikin jimillar mutum 660 ne da rahoton shekara na hukumar yaƙi da miyagun ƙwayoyi ya bayyana tare wasu daga ƙasashen Nepal (203), da Myanmar (25), […]

Babban Labari Labarai

Kungiyar Lauyoyi Ta Bukaci Mambobinta Su Yi Taka Tsan-tsan Wajen Yin Amafani Da Fasahar AI

Kungiyar Lauyoyi ta Najeriya NBA, ta buƙaci mambobinta da su yi taka tsan-tsan wajen amfani da sabuwar fasahar AI wajen samun bayanai domin inganta aiyukansu. Shugaban kungiyar reshen Jihar Kano shiyar Karamar hukumar Ungoggo, Barista Ahmad Abubakar Gwadabe, ne ya bayyana hakan, yayin wani taron wuni guda da kungiyar ta shirya don ilimintar da mambobinta […]

Babban Labari Labarai

Ba Za Mu Yi Mamaki Ba Idan Shugaba Tinubu Ya Fara Cin Bashi Daga OPAY – Dino Melaye

Tsohon ɗantakarar gwamnn jihar Kogi, Sanata Dino Melaye ya ce ganin yadda gwamnatin Najeriya a ƙarƙashin Bola Tinubu ke cin bashi, yana ganin gwamnatin za ta iya cin bashi daga kamfanin hada-hadar kuɗi na intanet wato Opay da moniepoint. Dino ya bayana haka ne a zantawarsa da tashar ARISE a ranar Litinin, inda ya zargi […]

Babban Labari Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Bayyana Alhini Kan Harin Da Yan Bindiga Suka Kai A Borno

Mataimakin Shugaban Kasa, Kashim Shettima, ya bayyana matuƙar alhini ga gwamnatin jihar Borno da mutanen Darajamal kan harin ‘yan bindigar da ya yi sanadiyyar rayukan mutane da dama a ƙaramar hukumar Bama. Shettima ya ce wannan lamari babban rashi ne ga jihar da kuma ƙasa baki ɗaya. A cikin sakon ta’aziyya da ya tura ranar […]

Game Da Mu

Gidan Radio da talabijin mai kawo muku labarai akan rukunoni daban daban. Da Hausa Muke Magana.

Yi Mana Imel: info@muhasatvr.ng

Tuntuɓi: +(234) 912 222 1000