• Home  
  • Tinubu ya nemi kotu a Amurka ta hana fitar da takardun zarginsa da safarar ƙwaya’
- Babban Labari

Tinubu ya nemi kotu a Amurka ta hana fitar da takardun zarginsa da safarar ƙwaya’

Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, ya nemi wata kotu a Amurka ta hana Ma’aikatar Shari’a ta Amurka (DOJ) da hukumomin FBI da DEA fitar da wasu takardunsa da ake dangantawa da zargin safarar miyagun ƙwayoyi da aka taɓa yi masa, a cewar lauyoyinsa. Gidan talabijin na Channels ya ruwaito cewa Tinubu ya shigar da ƙorafi […]

Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, ya nemi wata kotu a Amurka ta hana Ma’aikatar Shari’a ta Amurka (DOJ) da hukumomin FBI da DEA fitar da wasu takardunsa da ake dangantawa da zargin safarar miyagun ƙwayoyi da aka taɓa yi masa, a cewar lauyoyinsa.

Gidan talabijin na Channels ya ruwaito cewa Tinubu ya shigar da ƙorafi ne a wani shari’ar neman bayanai da wani ɗan gwagwarmayar neman gaskiya a Amurka, Aaron Greenspan, ya buɗe ƙarƙashin dokar ’Yancin Samun Bayanai (FOIA).

Greenspan na neman a ba shi cikakken fayil ɗin FBI da sauran bayanan binciken da suka shafi Tinubu, ciki har da wasu bayanan da suka danganci shari’ar kwace kusan dala 460,000 a Amurka a shekarar 1993.

Sai dai lauyoyin Tinubu sun ce fitar da waɗannan takardu na iya ƙeta haƙƙinsa na sirri, suna masu cewa ko da an taɓa bayyana wasu bayanai a baya, har yanzu yana da haƙƙin kare bayanan da ba a fitar da su ba.

Tinubu dai ya sha musanta aikata wani laifi da ya shafi zargin safarar miyagun ƙwayoyi.

Game Da Mu

Gidan Radio da talabijin mai kawo muku labarai akan rukunoni daban daban. Da Hausa Muke Magana.

Yi Mana Imel: info@muhasatvr.ng

Tuntuɓi: +(234) 912 222 1000

Manyan Labarai