Tinubu ya umarci ICPC ta yi bincike kan kafa hukumar bogi
Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, ya umarci hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa ta ICPC ta gudanar da bincike kan wata hukuma ta bogi da ake zargin an ƙirƙire ta ba tare da sahalewar fadar shugaban ƙasar ba. A cikin wata sanarwa da kakakin shugaban ƙasar Bayo Onanuga ya fitar, shugaban ƙasar ya umarci […]










