Home » Yadda Masu Ƙwacen Waya Sun Kashe Ma’aikacin Jami’a A Kano 

Yadda Masu Ƙwacen Waya Sun Kashe Ma’aikacin Jami’a A Kano 

by Muhammad Auwal Suleiman
0 comment

Masu ƙwacen waya sun kashe wani ma’aikacin Jami’ar Northwest da ke Kano, Buhari Imam, ta hanyar daɓa masa wuƙa a ciki. 

Rahotanni sun bayyana cewa ɓarayin sun ritsa shi ne a yankin unguwar Sheka da ke karamar hukumar Kumbotso, inda suka sossoke shi da wuka a ciki kuma suka kwace wayarsa, a ranar Laraba.

Kafar yaɗa labarai ta BBC ta ruwaito cewa malamin ya rasu bayan da aka garzaya da shi Asibitin Koyarwa na Malam Aminu Kano, a ranar Juma’a.

Kwamared Bashir Muhammad Shugaban ƙungiyar ma’aikatan jami’ar (NASU), wanda ya tabbatar da aukuwar lamarin ya buƙaci gwamnatin Jihar Kano da sauran hukumomi da su ɗauki tsattsauran mataki a kan kisan.

You may also like

Leave a Comment

Muhasa TVR kafa ce ta labarai mai cikakkiyar rajista wadda manufarta ita ce ilimantarwa, da wayar da kai da Inganta al’adun Hausawa da kuma nishaɗantarwa.
Muna nan a kan titin Guda Abdullahi gida mai lamba 19 a Farm Centre, jihar Kano.

Ra'ayi

Labarai da Dumi-dumi

©MuhasaTVR 2023. Ku nemi izini kafin yin amfani da duk abin da aka wallafa a wannan shafi

Are you sure want to unlock this post?
Unlock left : 0
Are you sure want to cancel subscription?