• Home  
  • Yadda Masu Ƙwacen Waya Sun Kashe Ma’aikacin Jami’a A Kano 
- Babban Labari - Labarai

Yadda Masu Ƙwacen Waya Sun Kashe Ma’aikacin Jami’a A Kano 

Masu ƙwacen waya sun kashe wani ma’aikacin Jami’ar Northwest da ke Kano, Buhari Imam, ta hanyar daɓa masa wuƙa a ciki. 

Masu ƙwacen waya sun kashe wani ma’aikacin Jami’ar Northwest da ke Kano, Buhari Imam, ta hanyar daɓa masa wuƙa a ciki. 

Rahotanni sun bayyana cewa ɓarayin sun ritsa shi ne a yankin unguwar Sheka da ke karamar hukumar Kumbotso, inda suka sossoke shi da wuka a ciki kuma suka kwace wayarsa, a ranar Laraba.

Kafar yaɗa labarai ta BBC ta ruwaito cewa malamin ya rasu bayan da aka garzaya da shi Asibitin Koyarwa na Malam Aminu Kano, a ranar Juma’a.

Kwamared Bashir Muhammad Shugaban ƙungiyar ma’aikatan jami’ar (NASU), wanda ya tabbatar da aukuwar lamarin ya buƙaci gwamnatin Jihar Kano da sauran hukumomi da su ɗauki tsattsauran mataki a kan kisan.

Game Da Mu

Gidan Radio da talabijin mai kawo muku labarai akan rukunoni daban daban. Da Hausa Muke Magana.

Yi Mana Imel: info@muhasatvr.ng

Tuntuɓi: +(234) 912 222 1000

Manyan Labarai