• Home  
  • ‘Yan Bindiga a Jihar Zamfara Sun Rage Kuɗin Fansar da Suka Ayyana da Fari
- Labarai

‘Yan Bindiga a Jihar Zamfara Sun Rage Kuɗin Fansar da Suka Ayyana da Fari

A karshe ‘yan bindigan da suka yi garkuwa da mutane 85 a ƙauyen Wanzamai da ke cikin ƙaramar hukumar Tsafe a jihar Zamfara sun amince su karɓi Naira 20,000 kan duk mutum ɗaya.

A karshe ‘yan bindigan da suka yi garkuwa da mutane 85 a ƙauyen Wanzamai da ke cikin ƙaramar hukumar Tsafe a jihar Zamfara sun amince su karɓi Naira 20,000 kan duk mutum ɗaya.

Sun kuma buƙaci hukumomi da su janye sojoji daga kauyen a matsayin wani ɓangare na sharuɗan sakin wadanda aka sace.

Sun ba da karfe 12 na daren jiya a matsayin wa’adin da suka ɗiba tare da yin barazanar kashe duk wanda ya kasa biyan kuɗi a kan lokaci ko kafin lokacin da aka kayyade.

Manema labarai sun tabbatar da cewa ‘yan bindidar sun yi barazanar cewa muddin ba a janye sojojin da aka tura ƙauyen Wanzamai ba za su ci gaba da yin garkuwa da mutanen ƙauyen.

Wani ɗan asalin yankin, Abubakar Na’Allah ya shaidawa manema labarai cewa, a wata tattaunawa ta wayar tarho ‘yan bindigar sun aike da sakon cewa za su karbi Naira 20,000 kacal daga kowane mutum a cikin mutane 85 da suka yi garkuwa da su a matsayin kuɗin fansa, la’akari da matsalar rashin kuɗi da suke ciki.

Na’Allah ya ce, “Tun da farko ‘yan fashin sun bukaci a biya su Naira miliyan 50 domin su sako mutane 85 da suka yi garkuwa da su wadanda galibinsu mata ne da kananan yara da suka je dajin neman ita ce a ranar Juma’ar da ta gabata.

Amma bayan tattaunawar da aka yi da su ne suka yi wannan ragi, saboda sun fahimci cewa dukkansu marasa galihu ne.

Game Da Mu

Gidan Radio da talabijin mai kawo muku labarai akan rukunoni daban daban. Da Hausa Muke Magana.

Yi Mana Imel: info@muhasatvr.ng

Tuntuɓi: +(234) 912 222 1000