Home » Zaɓe: Kotu ta soke nasarar da gwamnan Nassarawa ya samu

Zaɓe: Kotu ta soke nasarar da gwamnan Nassarawa ya samu

by Muhammad Auwal Suleiman
0 comment
Zaɓe: Kotu ta soke nasarar da gwamnan Nassarawa ya samu

Kotun sauraron ƙararraki zaɓen gwamnan Kano a jihar Nassarawa, ta umarci hukumar zaɓen jihar da ta janye shaidar samun nasarar lashe zaɓen gwamnan da Injiniya Abdullahi Sule na jam’iyyar APC ya yi a zaɓen da aka yi na ranar 19 ga watan Maris ɗin shekarar da muke ciki.

Sannan kotun ta umarci hukumar zaɓen da ta ayyana David Ombugadu na jam’iyyar PDP a matsayin wanda ya samu nasarar.

Wannan umarni ya fito ne daga bakin mai shari’a Ezekiel Ajayi wanda ya bayyana hakan a yau.

A yayin da yake bayyana jin daɗinsa, tsohon shugaban majalisar Dattawan ƙasar nan, Bukola Saraki, ya taya ɗan jam’iyyar tasu ta PDP murnar wannan nasara da ya samu a kotun.

Wannan hukunci na zuwa ne bayan an yi makamancinsa a nan Kano inda kotun ta ayyana Dr. Nasiru Yusuf Gawuna a matsayin wanda ya lashe zaɓen Kano, a maimakon gwamnan Kano, Injiniya Abba Kabir Yusuf wanda tuni ya tabbatar da shirinsa na ɗaukaka ƙara.

You may also like

Leave a Comment

Muhasa TVR kafa ce ta labarai mai cikakkiyar rajista wadda manufarta ita ce ilimantarwa, da wayar da kai da Inganta al’adun Hausawa da kuma nishaɗantarwa.
Muna nan a kan titin Guda Abdullahi gida mai lamba 19 a Farm Centre, jihar Kano.

Ra'ayi

Labarai da Dumi-dumi

©MuhasaTVR 2023. Ku nemi izini kafin yin amfani da duk abin da aka wallafa a wannan shafi

Are you sure want to unlock this post?
Unlock left : 0
Are you sure want to cancel subscription?