• Home  
  • Za a miƙa ƴan Najeriya da ake zargi damfara zuwa Amurka
- Labarai

Za a miƙa ƴan Najeriya da ake zargi damfara zuwa Amurka

Za a miƙa wasu ƴan Najeriya shida da hukumomin Amurka ke nema ruwa a jallo bisa zargin damfarar sama da mata 100 ta hanyar zambar soyayya a intanet daga Afirka ta Kudu zuwa Amurka a yau. Masu gabatar da ƙara a Amurka sun ce ana tuhumar mutanen da laifin damfara da kuma halatta kuɗaɗen haram. […]

Za a miƙa wasu ƴan Najeriya shida da hukumomin Amurka ke nema ruwa a jallo bisa zargin damfarar sama da mata 100 ta hanyar zambar soyayya a intanet daga Afirka ta Kudu zuwa Amurka a yau.

Masu gabatar da ƙara a Amurka sun ce ana tuhumar mutanen da laifin damfara da kuma halatta kuɗaɗen haram.

An yi sama da faɗi da sama da dala miliyan shida daga hannun waɗanda lamarin ya shafa, ciki har da ƴan fansho da ƴan kasuwa, waɗanda aka yi wa karyar alaƙar soyayya a intanet.

An kama waɗanda ake zargin shekara biyar da suka wuce a wani babban samame da aka kai kan wannan ƙungiyar masu aikata laifuka. Za a mika su ga jami’an tsaron Amurka a Cape Town

Game Da Mu

Gidan Radio da talabijin mai kawo muku labarai akan rukunoni daban daban. Da Hausa Muke Magana.

Yi Mana Imel: info@muhasatvr.ng

Tuntuɓi: +(234) 912 222 1000

Manyan Labarai