Za’a Fara Gasar Cin Kofin Zakaru Ta Nahiyar Turai

A daren yau Talata 17 ga Satumba za’a fara gasar cin kofin zakaru ta Nahiyar Turai na kakar wasan 2024/2025.

Cikin wani salo da ba’a taɓa ganin irinsa ba, ƙungiyoyi guda 36 ne zasu fafata, saɓanin a baya da aka saba ganin guda 32.

Inda duk rukuni zai sami ƙungiyoyi guda takwas. kowace ƙungiya dai zata fafata wasanni guda huɗu a gida, hudu a waje.

Real Madrid ce dai ta lashe gasar a kakar wasan da ta gabata.

Post masu alaƙa

Senegal ta lashe gasar AFCON ta 2025

CAF ta soma bincike kan hargitsin da aka samu a wasan Najeriya da Algeria

AFCON 2025: Nijeriya ta kora Aljeriya gida